This site offers you with different novels series from one writer, I hope this will educate and as well as entertain you..

ALHAKI NEH! (Page 11)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

        *ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

           Feb,2018.

    # WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com         
   
    Wattpad @Hama_gee

Page 11   
               
                   °
    Tun Zainab na makaranta Allah ya d'ora mata jarabar son Aminu,sau da dama takan fad'a ma Ummanta amma a kowane lokaci sai Umman nata ta kwantar mata da hankali kan cewa ta bari ya kammala karatun shi dan ba aure zaiyi ba yanzun. Ta bari in ya kammala zatayi wa Zuwaira magana sai asuka san yadda za'ayi not knowing that Aminu zai samu mata tun kafin ya kammala karatun. Ba zata suka ji auren Aminu ya taso,babu yadda  iya sai haquri amma Umman tasha fad'a mata cewa idanma bata samu shiga ata farko ba ai namiji mijin mace hud'u neh tunda tana sonshi.

     Zuwaira ceh ta d'an tab'a Adda Hansatu kafin tace "keh k'awata muna kan magana,Aminu dai ko zuwa dubamu bayayi tunda yayi auren nan". Adda Hansatu cikin zabura kamar an mintsineta tsabagen gulma tace "karki fad'a mun,yanzu rashin mutuncin matar shin harya kai ga hakan?". Zuwaira ta d'anyi guntun tsaki kafin tace "keh dai bari kawai,shiyasa ma nazo wajenki dan nasan baki rasa mafita wa mutum,dan nikam da harna fara tunanin zuwa gurin malami dan inaganin asirce min harnashi tayi".  Da sauri Adda Hansatu ta tareta "a'a haba Zuwaira ,gara da kika taho wajen nawa neman shawarar ma".

    Baki kawai Zuwaira ta sake tana kallon Adda Hansatu,Adda Hansatun ce ta cigaba "akwai mafita ai,mafitar kuwa itace kisa shi ya sake aure". Waro ido Zuwaira tayi tareda fad'in "aure dai!". Adda Hansatu tace "aure fa,inba hakan ba ta yaya zakiyi ki janyo kan d'an naki gareki,ai yanzu kina sa shi ya aure wacce kike so to an gama dan gabad'aya sai yadda kika ce za'ayi".


    Shiru Zuwaira tayi kamar me yin nazari sai kuma ta dawo da kallonta ga Adda Hansatu,tace "amma maganarki da k'amshin gaskiya k'awata",Adda Hansatu tayi murmushi kafin tace "kina wasa dani kenan". Zuwaira tace "ai daman sanin kine yasa nace bari na kawo kuka na gunki". Adda Hansatu tace "hakane sannan".

   Zuwaira ce tace "amma ba wannan ba,babban matsalar itace ina zanga idon Aminun ballentana har in taso mishi da wannan maganar? Kuma kin san ba ganin girmana yakeyi ba ballantana tunda inda yana ganin girman nawa da bazai rink'a yin abinda yake yin nan ba. Sannan wa nake da ita da zan had'ata da Aminun inma ya yardan?".

    Wani irin dariya Adda Hansatu ta sake wanda yasa har Zuwaira ta fara tsarguwa. Can dai tace "wannan duk ba wata matsala bace ai,kin ga anan zan iya ceh miki fad'uwa tazo daidai da zama dan Zainab ba k'aramin k'aunar Aminu takeyi ba,baki ga yadda ta sauya ba gabad'aya jin na ambaci sunan shi?". Zuwaira tace "tabbas kuwa,gashi Zainab kam 'yace ma sai abinda muka ceh". Adda Hansatu tace "kw'arai kuwa,maganar samun shi kuwa zuwa zakiyi har Bauchin ki gamu dashi,ki nuna mishi da gaske kikeyi tunda d'ankine zaibi abinda kike so koda dan gudun fushin ubangijin shi".



    Zuwaira tace "kema fa kince wani abun,dan kam gaskiya bazan zauna ina uwarshi ace kuma wata tana juya minshi ba,wannan ba zai yiwu ba wallahi",haka Adda Hadiza tayita zugata ita kuma kanta na huruwa harta yanke shawarar nanda sati guda zata je Bauchin. Bayan sun gama shawarwarinsu sai Adda Hansatu ta rakata sannan ta dawo gida.


   www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 10)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Jan,2018.

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Wattpad @Hama_gee

Page 10

°
K'arfe 3:30pm...
Zuwaira na zaune ta had'a uban tagumi,gabad'aya abin duniya ya isheta. Ta rasa yadda zatayi kan lamarin Aminu,gashi girma yake dad'a yi amma babu wata alamar canzawa a tattare dashi,hakan ba k'aramin tayar mata hankali yake ba. Gashi bata sake haihuwa ba balle tace inba wancen akwai wani. Hakan yasa ta fara mugayen tunani da shawarwari.

Akwai wata k'awarta ko ince aminiyarta dan tun suna yara suke tare,sunanta Hafsa ana ce mata Adda Hansatu. Itace ta fad'o ma Zuwaira a tunani,tashi tayi babu shiri ta sab'i hijabinta ta sanya. Ta rufo k'ofar ta fice,Mahdi baya gida balle ta sanar mishi zata fita,ko dayake ko yananan ma ba hanata zaiyi ba dan ta raina mishi dama.

Adda Hansatu na zaune tana kwashe tuwo dan da wuri take girginta itakam. Tana yi tana y'an wak'e-wak'en ta,sallamar Zuwaira da ta jiyo yasa tayi shiru tana sauraron me shigowa. Sallama Zuwaira ta sakeyi ita kuma ta amsa tareda yi mata iso. Shigowar Zuwaira yasa ta sake muciyar da ke hanunta ta taso da sauri tana yi mata maraba sannu da zuwa.

Har uwar d'aki ta kai Zuwaira sannan ta bata wuri ta zauna sannan ta fito ta lek'a d'akin Zainab 'yarta kenan tace tazo ta kawo ma bak'uwarta ruwan sha,saida Zainab ta gama mitarta tukun na ta tashi kai ruwan.

Bayan ta gama lallashi da rok'on Zainab saita koma d'aki gun Zuwaira,suka gaisa suna masu farin cikin ganin junansu dan sun jima basu had'u ba dama. Halinsu d'aya babu banbanci ko kad'an hakan yasa k'awancen su jimawa,itama Adda Hansatun sai abinda tace a gidan ake yi dan ita kanma bata zauna da uwar mijinta ba dan tace bazata iya ba,amma a halin yanzu uwar mijin batada rai.

Nan suka shiga gulmace-gulmace kan abinda be shafe su ba suna tafawa da dariya. Zuwaira ta gyara zama kafin tace "k'awata kin san ko abinda ke tafe dani?",Adda Hansatu tace "saikin fad'a". Zuwaira tayi gyaran murya kafin tace "maganar d'ana dai,Aminu!". Adda Hansatu tace "me kuma ya samu Aminu dake birni?",kafin Zuwaira ta bata amsa sai Zainab ta bankad'o labulen d'akin babu ko sallama ta shigo tazo ta ajiye ruwa da cup d'in da mamanta tace ta kawo.

Ba tareda tayi wa Zuwaira kallon mutunci ba tace "sannu da zuwa",kafin Zuwaira ta amsa kuwa ta juya kai zata fice,muryar maman neh ya dakatar da ita "baki ganeta bane Abuwa?,Maman Aminu ce fa". Zainab ta juyo tareda washe baki sannan tace "au,kin san ban ganeta ba Umma".

Ita dai Zuwaira kallonsu kawai take yi da mamaki,maganar da Zainab tayi ne ya dawo da hankalinta. Har k'asa Zainab ta tsuguna tareda fad'in "ina yini Umma Zuwaira". Zuwaira ta d'anyi murmushi kafin tace "lafiya lau 'yata,haka kika girma ai na jima ban ganki ba". Zainab tayi dariya tareda fad'in "ai Umma tace min kina tambayata in kinzo lokacinda nake makaranta". Zuwaira tace "yanzu kam anyi candy ai". Zainab tace "eh". Bayan sun gama Zainab ta tashi zata fita sai maman ta tace ta d'an k'arasa tuk'a mata tuwo a kan wuta daga nan saita kwashe,babu b'ata rai ko tura baki ko wani gunaguni dai tace "toh Umma" saita fice zuwa yin abinda uwar ta sata.

Ko kun san dalilin daya saka Zainab rusuna jin ance Zuwaira ceh? Ko me yasa ta rawar jiki? Ko miyasa da maman tasa ta wani aikin batayi hancini ba? Muje zuwa shafin gaba dan warware muku k'ullin...

     hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 9)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Jan,2018.

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Wattpad @Hama_gee

Page 09

°
Bayan wata guda hutun su ya k'are,so basu yi wasting time ba soka koma school suka cigaba daga inda suka tsaya. Kwanaki nata wucewa,soyayya da shak'uwa nata k'aruwa a tsakanin su. Kowa yasan Aminu a gidansu Amina,jira yakeyi ya kammala degree d'inshi kafin ya sanar a gida.

2yrs ltr...
Aminu ya auri Amina,suna zaune a nan Bauchi cikin kwanciyar hankali da samun nutsuwa a tsakani. Rayuwar su abin birgewa ce ga wanda ya gani. Yanzu Amina na 300 level kuma Alhamdulilah tana fahimtar karatun sosai,duk wani abinda ya shige mata duhu tana kawo ma Aminu,shi kuma sai yayi guiding d'inta.

Akwai wani hali guda na Aminu da Amina bata so ko kad'an,sai dai tayi-tayi dashi amma abin kamar yafi k'arfinta dan ya kada canzawa. Ba wani hali bane wannan illa halin rashin kulawa da iyayenshi,kwata-kwata bai damu dasu ba,baya wani zuwa dubasu while they so much need him this moment because sun fara tsufa,bayan nan basuda wani d'an bayan shi. Wannan shine babban damuwa a wajen Amina yanzu.

Yau suna zune a palour suna kallo bayan sallahr isha'i,Amina ta dubi Aminu cikeda kulawa ta kira sunanshi kamar yadda ta saba kira "hobby" ,Aminu ya amsa mata "na'am" tareda juyo kanshi gareta. Tace "yaushe zamu je gaidasu Umma kaga har mun kusada yin shekara guda da yin aure,kuma hakan bai kamata ba ace suna raye amma kwata-kwata baka kula da hidimarsu". Aminu ya maida kallon shi ga tv inda suke kallon wani Nigerian film a African magic Igbo. Saida ya d'anyi nazari kad'an kafin yace "nifa kin kasa gane mun ne kawai,amma ba wai bana son kula da hidimarsu bane,abin ne sai a hankali dan haka na taso babu wani sabo a tsakanin mu,even though ina iyaka k'ok'ari na tunda nake tare dake wajen ganin na gyara hakan".

Amina tace "to Allah ya kyauta,yanzu yaushe zamu je mu duba su?",yace "randa kike so ni yayi min amma ni bawai ina wani son zuwa bane dan bana musu kallon iyayena ma",da sauri Amina ta rufe mishi baki kafin tayi magana "haba don Allah,meyasa kake yin hakane? Iyayenka kake cewa baka musu kallon iyaye?",Aminu ya d'aga mata kai alamar eh,idon shi cikin nata babu ko k'yaftawa,ga hanunta a kan bakinshi.

Tasowa tayi daga k'asa ta dawo kan cinyarshi ta zauna tana shirin yin kuka,babu shiri ya gyara yace mata "kiyi hak'uri to me kike so inyi miki?",tace "kasa mana ranar da zamu je gaidasu Umma",cikin shagwab'a tayi maganar,shikuma da rawar jiki yace "angama,jibi zamu iya zuwa". A rayuwar shi baya son ganin b'acin ranta dan haka zai iya hak'ura da duk wani farin cikin shi dan samun nata.

Amina taji dad'in hakan sosai sannan tana rok'on Allah ya bata sa'a kan abinda take cimmawa. Tace "nagode hobby na" tareda hugging nashi,shima hugging d'inta yayi suna jiyo numfashin juna,ganin salon su na shirin saiyawa yasa na tattara takadda da biro na na waske🏃🏻‍♀️..

***
Washegari ta kama shirye-shiryen zuwa garinsu Aminu gaida iyayen shi. Ta sanar ma mahaifiyar ta,mahaifiyar tasa mata albarka tareda musu fatan alkhairi sannan tace mata ta k'ara dagewa da abinda take shirin yi dan aikin lada ne babba kuma Allah ya taimaka,daga k'arshe tace ta gaida mata Aminun kafin tayi hanging.

Aminu taji dad'i sosai tareda k'ara samun k'arfin gwiwa akan nada,sannan tayi alk'awari ma kanta na cewa duk rintsi duk wuya saita cimma burinta na had'a kan mijinta da iyayenshi,daga k'arshe take rok'on Allah ya bata nasarar yin hakan da kuma juriya da hak'urin yin hakan dan babban aiki ne..

   hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 8)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Jan,2018.

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Wattpad @Hama_gee

Page 08

°
Bayan sun iso SLT a dai-dai jikin wata bishiya akwai benches na zama so sai suka zauna a wajen shi kuma Aminu ya k'arasa ya shiga cikin SLT. Can sama ya hangota a zaune tana karatu,ga dukkan alamu ta gajiya tana son tashi ne don yaga tana tattara books d'inta dake kan desk d'in.

Hawa yayi har inda take zaune sannan ya nemi seat next to nata ya zauna tareda yi mata sallama. Ta amsa ba tareda ta kalleshi ko inda yake ba,yadda take abinta a nutse yana mugun birgeshi. Nan ya fara mata magana,ya sanarda ita dalilin zuwanshi da kuma inda ya fara ganinta da dai sauransu,sannan yayi mata introducing kanshi tareda nuna buk'atar itama ta gabatar mishi da kanta.

Bata wani bashi wahala ba saidai ita batace mishi ta amince da buk'atar shi a gareta ba. Amma yayi matuk'ar yin farin ciki tareda godema Allah da yasa ta yarda da shi duk da bata furta ba amma alamu sun nuna kansu. Nan Aminu ya taya ta had'a kan books d'inta tareda rik'o mata su,har kusada hostel ya rakota kafin ya bata books d'in sannan ya karb'i number d'inta tareda rok'on ta sanar mishi sunanta don daga farko bata fad'a mishi ba.

Nan ta bashi number tareda fad'in sunanta Amina amma Meena is her nickname dan amfi saninta ma ta hakan. Ya karb'a tareda yin godiya da yimata sallama sannan suka rabu zuciyar shi fal da farin ciki. A haka ya koma gun abokanshi ya sanar dasu yadda sukayi da ita,suma sunyi farin ciki sosai.

Amina Yaseen Ahmad (Meena) asalin 'yar Bauchi ceh,nan iyayenta suke kuma nan ne asalin su. Tana da yayyu uku,biyun farko maza neh sai yarta wacce take bi me suna Aisha,sa'annan tana da k'anne guda biyu ,namiji me suna Abdallah sai Aneesa wato 'yar autar su kenan. Su shida kenan a wajen iyayensu,babban yayansu me suna Aliyu yana da aure da d'anshi d'aya dan shekaru biyu kenan da auren nashi. Second born d'in kuma wato Auwal yana service d'inshi a Benue. Sai Aisha wacce Amina ke binta tana 400level anan ATBU,I.T kenan. Tanada aure da yaran ta biyu.

Sai Abdallah na SS2 yanzu,sannan Aneesa autarsu kenan tana Jss1. Kad'an daga tarihin Amina kenan..

***
A week ltr..
Da daddare wajen 8:30 Aminu ya kira wayan Amina inda suka sha hiransu kafin sukayi sallama daga baya. Soyayya ta k'arfi a tsakanin Amina da Aminu cikin k'ank'anin lokaci wanda hakan su kansu yana basu mamaki,hakama ga mutane dan dukansu ba masu hayaniya bane. Yawancin lokuta suna tare ko suna hira ko suna karatu,dan ya kan koya mata abubuwan da bata ganesu ba.

A kwana a tashi babu wuya,har suna shirin gama first semester exams,karatu kowannen su yasa gabanshi dan haka yanzu sun rage had'uwa ma,yawanci suna venue suna karatu. Amina ta riga shi gama exams dan haka bayan ta gama gida ta koma,kullum suna waya duk da ba sosai dan baya samun lokaci sosai amma tana bashi uziri dan tasan yanayin karatun nasu saida dagewa da naciya inba haka ba bazasu samu abinda suke so ba.

Bayan gamawanta da one week shima ya kammala nashi,a ranar ya koma gida dan da safe yayi exam d'in. Da daddare kuwa yaje wajenta,sun jima suna hira kafin yayi mata sallama ya koma gida. Bayan komawar shi gida saida sukayi waya kafin sukayi bacci.

    hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 7)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Jan,2018.

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Wattpad @Hama_gee

Page 07

°
A dai-dai k'ofar Maharaj (restaurant) ya tsaya ganin sun riga sun iso,dan daga gani a Zion (sunan hostel) take saboda babu wani hostel gabada da wannan. Sai da ya jira yaga shiganta kafin ya yi gaba dan shima hostel d'insu ta wajen ake bi. Ranan Aminu ya sha mafarkai dan ba k'aramin kamuwa da son yarinyar nan yayi ba.

Washegari tun bayan sallahr asuba Aminu ya nufa Science Lecture Theatre (SLT) dan yin karatu saboda already sun fara test,kuma yauma sunada wani k'arfe 2. Bai bar hall d'innan ba sai k'arfe 9 na safe,ya taso kenan yana saukowa saiga yarinyar jiyannan ta shigo ita kuma tana hawowa dake steps neh wajen.

Tsayawa yayi cak harta zo ta wuce ta gefen shi,jikin shi yayi matuk'ar yin sanyi harma ya rasa abinda zaiyi,nan ya fara tunani yaje ne ko ya barta ba yanzu ba tunda karatu zatayi karya hanata yi. Daga k'arshe dai ya yanke shawarar tafiya inyaso in yaje ya karya saiya dawo kafin nan ta gama karatun,hakan kuwa yayi.

Nan ya ja jikin shi yabar cikin SLT yazo ya tsallaka titi ya shiga hostel. Bayan ya shiga d'aki ya ajiye takardun dake hannun shi ya d'an zuna a gefen katifar shi yana wani nazarin. Sulaiman abokin shine yayi sallama ya shigo,Aminu bai ma ji sallamar ba dan tunani da sak'e-sak'e yake tayi,Sulaiman ya dube shi kafin yaje ya sauk'e abinda ke kan wuta dan harya fara kamawa duk Aminu na zaune a d'akin kuma bai ji ba.

Bayan ya sauk'e sai ya dawo gareshi tareda yi mai tambayar "lafiyar ka kuwa?",sai lokacin Aminu ya san da shigowar shi,yace "ah! Yaushe ka shigo kai kuma?". Sulaiman yace "ina zaka sani ka zauna nan kana ta tunani". Aminu yace "bari kawai wallahi".

Sulaiman yace "gashi ka d'ora girki harya fara k'una,amma na dauk'e maka",Aminu yace "anya kuwa,bani na d'ora ba inajin nima na shigo na sameshi don banma san dashi ba". Sulaiman yace "ba mamaki Sadiq ne to,yanzu haka ya d'ora ya tafi d'akinsu Ustaz don ina wucewa na jiyo shewarsu". Aminu yace "maybe".

Suna cikin haka saiga Sadiq yayi sallama ya shigo d'akin tareda fad'in "subhanallah,harya fara k'una". Sulaiman ya harare shi tareda fad'in "kai dai you never change wallahi,ace mutum ya d'ora abu inba ganganci ba ya tafi ya bari kuma babu kowa a d'akin". Sadiq yace "da nasan hakan zata faru neh? Kuma ma ba don ku nake girkin ba wai karku dawo ku nemi abinci".

Aminu dake shi yana biyewa Sadiq d'in yace "don't worry my aboki,leave him ai kayi k'ok'ari". Sulaiman ya ja tsaki tareda mik'ewa ya basu waje,ai kuwa dariya sukayi mishi,nan Sadiq yayi serving d'insu suka zauna suka fara ci,da k'yar Sulaiman ya hak'ura ya jona su suka ci abincin. Bayan suna gama ne Aminu take basu labarin yarinyar nan tun daga ganinta jiya zuwa yau dan bashi da wasu abokai da suka wuce Sadiq da Sulaiman.

Sadiq ne ya dubeshi yace "ai kuwa tashi zakayi yanzun nan muje mu tsaro ta,koya kace" ya k'arasa yana kallon Sulaiman,shi kuma Sulaiman d'in harda gwaleshi tareda fad'in "kaifa ka fiye rawar k'afa,wane irin kuje ku tsaro ta,shi dai yaje ya tsara abinshi haka yafi". Sadiq yace "kaima kace wani abu" ya juyo ya kalli Aminu kafin yace mishi "tashi zamuyi yanzu mu raka ka amma ki zaka k'arasa kayi mata magana,in yaso daga baya idan kun daidaita ma gaisa muma ko", Sulaiman yace "yanzu kayi magana mutumi na". Ya bashi hannu suka tafa,nan suka fice tareda zuwa SLT.



     hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 6)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Jan,2018.

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Wattpad @Hama_gee

Sorry for the late post🙏

Page 06

°
Mahdi ya d'an sassauta rashin mutuncin da yake yida Kawu Bello dan yanzu har zuwa gaishe shi yakeyi, shima Kawu Bellon ya d'an sauk'o saidai ba sosai ba. Kusan ance me hali baya dainawa,koya rage shi dai yana nan dan bazai iya daina shi ba,to Zuwaira na nan akan bakan ta na wulak'anta mutane,musamman ma y'an uwan Mahdi.

Tun bayan rasuwar mahaifiyar Mahdi aka gyara d'akinta ma Aminu dan ya fara wayo,gashi da hankali da hangen nesa. Aminu yaro ne me ban sha'awa,yasan mutuncin mutane duk da yanayin mahaifiyar tashi. Sai dai wani hanzari ba gudu ba,Aminu ya taso babu wata shak'uwa a tsakanin shi da iyayen nan nashi guda biyu,barin ma Zuwaira dan yafi zama da Baban akan da ita.

Hakan yasa ya taso bai damu dasu ba,hakanan suma d'in. Wannan shine babban kuskure da iyayenshi suka sake tafkawa a karo na biyu. A sannu a hankali yana zuwa makaranta yana k'ara girma da wayo,har ta kaimu yanzu Aminu yana aji shida a makaranta secondary. Kuma a halin yanzu bai wuci saura y'an watanni su zana jarabawar kammalawar su ba. Hakan yasa shi k'ara dagewa a karatunshi daman yana k'ok'ari sosai a makarantar.

Wani abin birgewa ma shine,tun yana aji uku amatakin secondary ya haddace alqur'ani me girma,ta ko'ina dai ba'a barshi a baya ba kama daga bokon har islaman. Wannan kuma shine babban gatan daya samu daga wajen iyayenshi.

Bayan shekara guda.
Aminu ya gama secondary school,har result ya fito kuma yayi kyau dan JAMB d'inshi ya samu 190points,WAEC kuma duka ya samu credit. Sannan Industrial design ya cika a matakin degree a Abubakar Tafawa Balewa University Bauchi (ATBU) dake akwai k'anin kakanshi wato k'anin Baban Mahdi.

Tun Aminu na matakin secondary yayi wa Babanshi magana kan idan ya kammala yana so ya d'aukeshi ya saka shi a makarantar gaba. Allah me yin yadda yaso kenan,har yau har gobe Zuwaira bata sake haihuwa ba in banda b'ari da tayi shekaru hud'u da suka wuce,yanzu ko b'arin ma babu,Aminu neh idon ganinsu duka.

Aminu kuwa ya dage da karatunshi dan ya riga ya saka ma ranshi cewa karatun ne gatanshi. Lokaci lokaci ya kan lek'asu idan ya samu hutun makarantar. Duk da wahalar da ATBU kedashi hakan bai rage mishi k'warin gwiwa ba saima k'ara dagewa da yakeyi.

A kwana a tashi babu wuya,Aminu na final year a ATBU. Watarana yana karatu a library yaga shigowar wata 'yar budurwa,tunda ya shiga makarantar bai tab'a tsare wata yarinya da sunan tayi mishi ba,in fact bai tab'a soyayya ba baima da lokacin yinta,sai dai ya zamo dole ya karya record yau dan ba kad'an ba yaji yarinyar ta kwanta mishi a rai.

Sanye take da atampa sai dai ba lallai kasan wane irin d'inki bane dan himar ne dogo a jikinta,doguwa ce amma ba sosai ba,bata da k'iba ko kad'an. Sannan daga ganinta kaga farar mace,tana da kyau dai-dai misali. Sannan da fara'a cike a fuskarta,daga ganinta kaga fresher ma'ana sabuwar shiga daga yanayin tafiyarta na rashin sabawa da wurin.

Can Aminu ya dawo daga tunanin da yakeyi,wajen 9:30pm yaga ta taso zata bar wajen.Babu shiri shima ya kwashe kayanshi yabi bayanta duk da cewa ba lokacin yayi niyyar fita ba,yaso ace ya kai koda 10 ne amma dai ya fito.Tana tafe yana binta sai dai ya kasa mata magana ganin dare yayi kuma daga gani sauri take ta koma hostel.

Shi dai yarinyar ta birgeshi ganin yadda takeda nutsuwa,daga gani bata shiga shirgin k'awaye dan bai ganta da kowa ba.

     hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 5)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Jan,2018

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Wattpad @Hama_gee

Ina me k'ara bawa masoya da ma'abota karanta littattafai na a duk inda kuke hak'uri kan jina da kukayi shiru kwana biyu,naga sak'onninku kuma nagode Allah ya bar zumunci da k'auna. Na samu hutun makaranta so insha Allahu zamu cigaba daga inda muka tsaya... Daga k'arshe ina muku fatan alkhairi,Happy new year...

Page 05

°
Wajen k'arfe bakwai na safiyar yau Zuwaira ta gama d'umama sauran tuwon da suka ci jiya akan zasu karya dashi yanzun. Ta raba ta sama kowa nashi sannan ta kira Aminu yazo ya d'auka ma Babanshi nashi ya kai,ita kuma ta d'au na Umma ta nufa d'akinta dan kai mata. Ganin har yanzu tana bacci yasa ta tab'e bakinta tareda fad'in "sabon salo,inba lalaci ba me zaisa har yanzu ace mutum bai tashi daga barci ba",tana kaiwa nan ta juya ba tareda tashinta ba.

D'aukan nata tayi sannan ta nufa k'ofar d'akinta inda ta zauna ta fara cin tuwon.Bayan sun gama sai Mahdi ya shirya ya tafi kasuwa,Aminu kuma makaranta ya tafi saiya rage saura Zuwaira ita kad'ai a cikin gidan. Itama bayan ta gyara gida tayi wanke wanke saita kwanta bacci,ba ita ta tashi ba sai wajen sha biyun rana.

Ta fito waje tareda neman kujera ta zauna kafin ta ware a baccin tasan me zata dafa musu na rana. Kukan akuya ta jiyo a d'akin Umma shine ya juyo da hankalinta wajen,ganin bata ji Umma ta koro akuyar ba yasa ta tashi taje dan ganin ko Umman bata ciki neh.

Tana shiga kuma taganta a cikin d'akin kwance a kan shimfid'ar ta kamar yadda tazo d'azu ta ganta. Abin ya d'aure ma Zuwaira kai sosai,nan ta shiga tashin ta amma ina shiru kake ji. Ta d'aga hanunta taji baya motsi kuma bata numfashi,nan ta tabbatarwa kanta cewa Umma ta mutu. Abinka da zuciya kuma ta musulunci dole ta d'anji wani abu ganin gawar Umma,saidai bai wani dameta sosai ba.

Tashi tayi ta nufa k'ofar gida wurjajan kamar an korota,tayi kiran wani yaron makw'aftan su sannan ta aikeshi yaje ya kira mata Mahdi a kasuwa,da gudu yaron yaje aikan kasancewar yadda tajaa mishi kunne kan yayi saurin.

Bayan kaman 15mins da aiken yaron saiga Mahdi ya dawo gida dake akwai y'ar tafiya daga kasuwar zuwa gida kuma ba abin hawa gareshi ba. Yana shigowa Zuwaira ta ruga inda yake da gudu tana kuka tana nuna mishi d'akin Umma,a zatonshi ma wani abun Umman tayi mata,tambayarta ya shiga yi "lafiyarki,meya faru?". Zuwaira dai yau babu bakin amsawa sai janshi da tayi har izuwa d'akin. Suna shiga ta zube a k'asa gaban Umma tana zuba kuka.

Anan neh hankalin Mahdi ya soma tashi dan tunanin da yazo mishi a rai sanda ya ganta,shima tsugunawar yayi kisada ita yana kiran sunanta "Umma! Umma lafiya kuwa,meya sameki?",kuka ya shiga yi kamar mace. Sai lokacin Zuwaira ta dubeshi dan taga kamar be fahimci halinda Umman ke ciki bane,tace "Mahdi saidai hak'uri fa dan Umma ta riga mugidan gaskiya",ta wani jaa numfashi bayan ta fad'i hakan.

Wani dummm Mahdi yaji,kanshi ya d'au zafi saidai babu yadda zaiyi tunda dama mutuwar dolece kuma kowa ma zaman jiranta yakeyi. Nan ya tashi ya fita yayi kiran mak'ota akazo ana k'ok'arin yi mata wanka. Kafin nan saiya tafi gidan Kawu Bello dan sanarda shi rasuwar,yaci sa'ar samun shi a gida kuwa saidai daga farko korarsa yayi da cewa karya yadda ya shigo mishi gida kuma karya yadda ya sake zuwa koda ta layin gidanshi neh.

Saidai jin maganar dake tafe da Mahdi yasa shi jin sanyin jiki,gabad'aya ya rasa samun nutsuwa. Tare suka koma gidan inda suka tarar har anyi mata wanka,nan aka sanar a masallaci tareda yi mata sallah a masallacin juma'a. Bayan an kammala komai sai aka d'auketa aka kaita kabari. _*Allahu akbar,Allah kasa muyi mutuwar shahada,kasa muyi dace da samun rahamarka dan darajar al'arshi,ameen*_.

Bayan an kaita anyi mata addu'o'i sai kowa ya dawo gida,aka bar y'an uwa da koke koke. Nan aka shiga dafe-dafen abincin bak'i y'an gaisuwa. Haka ranar ta kasance musu babu dad'i.

Washegari ma an karb'a bak'i sosae,masu zaman makoki da kuma masu zuwa ta'aziyya su fita duk dai gasunan. Haka aka jera kwana uku anayi. Abu kamar ba zai wuce ba,yau kimanin sati guda kenan da rasuwar..

    hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 4)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Sept,2017.

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Wattpad @Hama_gee

Ina me baku hak'uri kan rashin jina da wuri,wata matsala aka d'an samu amma yanzu komai ya daidaita insha Allah.Hamagee loves u all #Team AHN👏👋

Page 04

°
Kai tsaye Mahdi ya nufa gidan Kawu Bello babu wani shayi,da isar shi kuwa ya hau doka sallama "salamu alaikum!,salamu alaikum!!,salamu alaikum!!!".Kafin a fito ya k'ara wata sallamar kafin yace "wai babu mutane ne a gidan nan?",can saiga wani yaro ya fito da gudu yana "waalaikum salam".Mahdi ya dube shi cikeda takaici yace "tun d'azu nake sallama kaman babu kowa a gidan,ina Babanka?".

Yaron ya dubeshi yace "yana ciki shine yace nazo na duba waye ma,ka shigo".Mahdi yace "duba! Ni ba shiga bace ta kawoni,yi min kiran Baban ka kawai!".Yaron yace toh sannan ya juya da gudu kamar yadda yazo.Cikin mintuna da basu wuce biyu ba da shigan shi ba saiga Kawu Mahdi ya fito sanye da babbar riga.

Ganin Mahdi a tsaye a wajen ya bashi mamaki,yace "lafiya kazo gidana ka tsaya a waje kamar wani bak'o?",Mahdi yace "lafiya lau" a tak'aice.

Kawu Bello yace "to madallah,daman ina neman ka kaga kuwa kazo a daidai".Mahdi ya dubi Kawu Bello yace "ni ba wannan bane ya kawo ni wajenka,naji abinda kaje gida kayi wa matata Zuwaira kuma ka kyauta",cikeda mamaki Kawu Bello ya saki baki yana kallon Mahdi dan be tab'a tunanin rashin mutuncin nashi ya kai haka ba,saidai wani sa'in baya ganin laifin shi dan a cewarshi Umma ceh ta b'ata shi.

"Lallai Mahdi yau ka tabbatar mun da rashin hankalinka a fili,ni kake yiwa irin way'annan kalaman?",Mahdi yace "Kawu kenan,wai a daki mutum kuma a hanashi yin kuka.Koma miye ni ba damuwata bace,damuwata d'ata kuma itace ka daina zuwa gidana kana zagin matata dan bazan lamunta ba wallahi".

Kawu Bello yace "hakane,yanzu ka tabbatar mun da cewa mace tafi iyayenka daraja a wajenka,ni dai bazan maka baki ba amma ka sani komai daren dad'ewa zaka girbi abinda ka jima kana shukawa,wannan itace maganar dan haka ka wuce ka bani waje bani ba kai kaje can ka k'arata da matar taka amma ni na cire hanuna akanka kuma insha Allahu zan d'auki Yaya daga wajenku kafin bak'in cikinka da matarka ya k'arasa ta,ja'iri kawai".

Kawu Bello na kaiwa nan ya bar Mahdi a wajen ya shige gida a fusace.Shima Mahdin barin wajen yayi,kai tsaye ya nufa gidanshi yaje ya k'are cin mutunci wa Umma kafin ya dawo wajen Zuwaira ya cigaba da bata hak'uri.

******
Haka rayuwarsu ta cigaba da kasancewa har Allah ya kawo mun shekaru hud'u yanzu.Aminu yana tafiya kuma yayi wayo sosai,ga surutu dan har an saka shi a makarantar allo.Saidai har ila yau Umma tak'i komawa gidan Kawu Bello ita a dole tana son mutuwa a kusa da d'anta duk da cin mutuncin da yake biye matarshi sukeyi ma.

Watarana da rana,Aminu ya nufa d'akin Umma da abincin shi wai suci tare kasancewar yadda yake son zama kusada ita dukda tsangwamar da Zuwaira keyi mishi in ta ga hakan.Abunka da yaro,besan me takeyi bama.

Ya zauna kenan suna cin dambu dan yau shi akayi a gidan,Zuwaira ta k'are neman shi a cikin gidan bata ganshi ba,hakan yasa tayi tunanin ko ya shiga d'akin Umma.Kai tsaye ta nufa d'akin taci sa'ar samun shi kuwa yana zaune suna cin dambu ita kuma tana mishi hira kamar wani sa'ar shi,abinka da kaka.

Finciko shi Zuwaira tayi tana fad'in "da wannan tsohuwar k'azamar kake cin abinci Aminu?,baka san hakan zai iya cutarda kai bane,to kada na sake ji ko ganin hakan ka jini?",ta zare mishi ido,ya d'aga kai alamar yaji sannan taja shi tana masifa.

Rayuwar duniyar ta ishe Umma,babu d'a babu jika kowa yana gudunta.Dama Kawu Bello neh kuma shima ya daina taka k'afarshi gidan sakamakon rashin mutunci da cin zarafin da Mahdi yaje har gidan shi yayi mishi dama akwai shi da zuciya.

Shekaru sunata k'arewa,tsufa yana ta k'aruwa mata.Aminun ma da yake zuwa wajenta tana jin dad'i yanzu ya daina dan ya fara wayo kuma Zuwaira ta riga ta sa mishi k'inta a ranshi.Kullum ita kad'ai take zama a d'aki yanzu,ga wulak'ancin da take sha a wajen Zuwaira kuma babu yadda ta iya tunda d'an nata ma baya ganin kimarta balle matar ta gani.

5yrs ltr,
A kwana a tashi,asarar me rai inji Mallam Bahaushe,yau an wayi gari babu ran Umma.Allah yayi mata cikawa a daren yau wato Juma'a,ta idar da sallahn dare kenan kamar yadda ta saba kullum duk da kasancewar ta tsufa sosai dan da ky'ar ma take iya tashi.

Ta idar da sallahn kenan tayi addu'o'i ta shafa sa'annan ta nemi gu ta kwanta,toh tashin da bata yi ba kenan a wayewar garin yau.Masha Allah,Allah yayi ma Umma cikawa,ta huta da muzgunawa irin na Zuwaira.

Ko yaya zasu k'are? Muje zuwa dai👌😱..

     hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 3)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

*K'UNGIYA MAI SUNA A SAMA WATO P.M.L.W SUNYI SHIGE DA FICE WAJEN KAWO MUKU HANYOYI MAFIYA SAUK'I DA ZAKUNA BI DAN SAMUN LITTAFANSU KAI TSAYE,WAY'ANNAN SHAFUKAN KUWA SUNE WANDA ZAN JERO SU A K'ASA.BUK'ATARMU KAWAI ITACE KU CIGABA DA BINMU DAN MU NAKU NE,SANNAN KADA KU MANTA A KODA YAUSHE IN KUN KARANTA KU RINK'A LIKING,COMENTING DA KUMA SHARING..SAI KUNZO....Mune dai PML Writers* 👌🏼

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# IG PML WRITERS
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Wattpad @Hama_gee

16th Sept,2017

Page 03

°
Jiki a sanyaye Zuwaira ta bar wajen da d'anta,ta koma d'aki ta soma kuka d'anta nata kallonta shima d'in ya fara kukan.

Kawu Bello kuwa ranshi yayi mugun b'aci,da ace yanada ikon da zai saka Mahdi ya saki Zuwaira toda ya jima da yin hakan dan babu abinda Zuwaira ta sanya a gaba sai muzguna ma Umma,kuma Mahdi na gani amma baya cewa komai.

Saida ya nemi gu ya zauna kafin ya dubi Umma ya kirata "Yaya",ta amsa da "na'am".Yace "a gaskiya na gaji da irin wannan zaman naki a gidannan,ace ke kenan kika rage mun a duniya amma ina ji ina gani ana k'untata miki?,toh gaskiya yau kam dole zaki bar gidannan inyaso Mahdin sai ya ringa zuwa koda kuwa kullum neh kina ganinshi tunda ba zai iya rabuwa da matarshi ba".

Umma tace "ka daina wannan maganan Bello,na riga da fad'a maka cewa anan gidan zan k'arasa rayuwata,me nake nema yanzu? Babu daman zaman jiran mutuwata kawai nakeyi to meyasa zan buk'aci wani jin dad'i na duniya,ka barni kawai dan babu inda zani".

Babu yadda Kawu Bello beyi da ita ba amma firr tak'i,haka yana ji yana gani ya barta a gidan.

****

Around 2:30pm Mahdi ya shigo gidan,kai tsaye d'akin Zuwaira ya shiga kamar yadda ya saba.Samunta yayi a kwance tasha kukanta harta gaji sannan tayi bacci,ga Aminu a gefenta shima yayi baccin.

Be tasheta ba ya nufi kitchen ya d'auko abincin shi dan yunwa yake ji a lokacin.Bayan ya d'auko saiya zauna yaci ya sha ruwa kafin ya tattare kwanukan ya mayar su zauren.

D'akin Umma ya nufa ya gaida ta sannan ya dawo d'akin Zuwaira shima ya kwanta,bai jima ba bacci ya d'auke shi.

Wajen k'arfe uku da rabi Zuwaira ta tashi,juyawan da zatayi sai taga Mahdi kwance yana bacci.Tashi tayi taje tayo alwala sannan ta dawo ta tashe shi kafin ta fara sallahn.

Bayan ta idar kuwa bata tashi a inda take ba har Mahdi ya shigo gidan.Zama yayi a gefen gadon yana jiranta dan a zatonshi ko addu'a takeyi.

Ga mamakinshi saiya ga har yanzu bata ko motsa a inda ya shigo ya sameta ba,kuma yasan in dai addu'a Zuwaira zatayi to bata wuce mintuna biyu gashi yanzu ta kusan mintuna goma tana zaune.Tasowa yayi yazo inda take zaune ya tsuguna a gabanta sannan ya dubeta.

Ya bud'i baki zaiyi magana saiya ga idonta cikeda k'walla tana k'ok'arin sharewa,yace "lafiya Zuwaira kike kuka?".Bata ce mishi komai ba hasalima kanta na kallon k'asa kamar yadda yazo ya sameta.Sake tambayarta yayi "lafiya Zuwaira,meya sameki?".

Cikin kuka ta fara fad'a mishi k'arya da gaskiyarta wai Kawu Bello neh yazo har cikin gidan ya zazzageta babu abunda ta mishi,saidata gama tsara mishi k'arerayinta sannan ta fashe da kukan gaske,shi kuma an tab'o mishi shalelenshi dan haka ranshi ya b'aci.

Nan ya shiga bata hak'uri yana lallashi har tayi shiru,tareda yi mata alk'awarin hakan bazai sake faruwa ba dan ya tabbatar mata da cewa zai je ya samu Kawu Bello suyi wacce za suyi yau d'innan,har cikin ranta kuwa taji dad'i.

Bayan nan ya tashi ya nufa gidan Kawu Bello kai tsaye.

    hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 2)

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Wattpad @Hama_gee

10th Sept,2017

Page 02

°
"Ina fa lafiya,wai ni don Allah Umma yaushe zaki daina takura ma Zuwaira neh? Me tayi miki haka neh?",Umma ta dubi Mahdi tace

"Me nayi mata?ita tace maka nayi wani abun ko kuwa?",Mahdi bbu koh kunya ya dubeta yace

"Ba kiyi mata komai d'in bane?,nifa gaskiya bana son irin abunda kike mata",Umma dai bata ce komai ba dan ganin yanayinshi,tasan tabbas inta matsa zai zageta shiyasa ta jaa bakinta tayi shiru.

Ganin hakan yasa Mahdi barin d'akin yana banbami.

Zuwaira kuwa ji takeyi kaman an tsundumata a aljanna tsananin murna,fitowar Mahdi yasa ta daina rawa da tsallen da takeyi.Ta wani marairaice kafin tace

"Yi hak'uri megida,karka sa damuwa a ranka da Allah".Ta ja shi suka shiga d'aki tana kanainaye shi da zantuka masu sanyaya zuciya.

****
Umma kuwa kwanciyarta tayi dan ta rigada ta saba da irin wannan yanzu,gashi k'aninta yayi yayi da ita ta koma gidanshi da zama amma firr ta k'i,k'aninta me suna Kawu Bello.

Shi kad'ai ya rage mata a rayuwannan,babu iyaye babu yayye kuma babu wasu k'annen,sai d'a d'aya tilo.Hakan yasa bata k'aunar rabuwa dashi koh kad'an dukda irin wulak'anci da tsangwamar da take fuskanta a gidanshi.

Babban abun takaicin ma wai harda shi d'annata ake ci mata mutunci,da iya matarshi ceh me yi mata hakan da da sauk'i amma dukansu.Ita kam taga rayuwa,kuma da ba haka yake ba.

Kuma babu alamun asiri a tattare dashi,kawai irin sonda yake ma Zuwaira neh yasa shi yake yin komai.Amma koma miye ita dai tana mishi addu'ar shiryuwa tareda matarshi.

Sallamar Kawu Bello ta jiyo dan hakan ta tsaya tsak da tunaninda takeyi tareda k'ak'alo fara'a a fuskarta.Yana shigowa kai tsaye d'akinta ya nufa dan daman wajenta yake zuwa tunda su Mahdi kam saidai suje gaidashi.

"Assalamu alaikum",ya fad'a a daff k'ofar shiga d'akinta.Ta amsa mishi da "wa'alaikum salam,Bello neh yau a gidannan,shigo mana".

"Nine yaya",ya fad'a tareda shiga d'akin.Neman guri yayi ya zauna,itama ta tashi ta zauna kafinnan suka shiga gaisawa.

Sun gama gaisawa kenan saiga Mahdi da Zuwaira sunzo gaidashi suma,har k'asa Zuwaira ta tsuguna tana gaidashi baki a yashe kamar da gaske,Umma dai girgiza kai kawai tayi ganin irin tadda Zuwaira ta k'ware a munafurci.

Bayan sun gaidashi sai Zuwaira ta tashi ta tafi d'akinta,Mahdi kuma zama yayi suka d'anyi wasu maganganu kafin ya tashi shima ya bita,bayan fitarsu neh yake tambayar Umma koda wata matsala,tace mishi babu.Daga bisani yayi mata sallama ya tashi ya tafi.

Bayan ya fito neh ya had'u dasu a waje sukayi sallama kafin ya wuce.

****
Bayan sati uku,
Kamar wasa Kawu Bello yake cewa bari yaje ya dubo yayarshi danya jima baije gunta ba,kamar zaije kamar kuma ya bari sai gobe dan akawai wajenda yake son zuwa yau d'in.

Kamar wasa dai saiya kama hanyar shi ta zuwa gidan,abunda ya tarar a gidan ba k'aramin b'ata mishi rai yayi ba.Wai Aminu ne yaje d'akin Umman yana wasa,itama wasan take mishi dan a rayuwarta inda abunda tafi k'aunarsu sune Mahdi da kuma Aminu jikanta.Sonda take ma Mahdi shiya shafi d'anshi amma duk baya gani idonshi ya rufe da son zuciya da biyewa mace.

Har yayi sallama ya shiga Zuwaira ba taji ba tsaban masifa da tijarar data tsaya yiwa Umma.Ranshi a bace ya k'arasa shigowa ya nufa inda suke,har yanzu Zuwaira bata san ya shigo dan sai masifa take tayi

"kurwan d'ana kurr in gaya miki,kin lallab'a kinga idona baya gurin shine kika je kika d'aukoshi samun kiyi mishi wani abun,to nafi k'arfinki in gaya miki.Kuma duk wani makirci da rashin mutunci irinnaku na sirakai na sanshi dan haka bazan tab'a yadda dashi a gidannan ba ehee,sannan......"

Bata k'arasa ba Kawu Bello yayi caraf yace "ya isheki haka keh,marar mutunci wanda bata san darajar na gaba da ita ba,kedai wallahi Mahdi beyi saan mata ba,tir da keh da masu irin halinki,inba rashin mutunci ba Yaya batayi sa'a da uwarki bane? Ko baki darajata dan uwar mijinki ba ai kya bata darajar ta haifeki.Dama tunda nazo ranan nasan baki dena mata tijara ba kawai dai tace mun babu komai nayi shirune amma ba wai na yarda ba".

Kamar mutuniyar arzik'i tayi shiru,kai kace ba ita ke zazzage masifa yanzu ba.Bayan ya gama da ita yayi tsaki ko amsa gaisywarta ma beyi ba ya shige d'akin Umma dake ta faman share k'walla tana fad'in yayi hak'uri ya k'yale Zuwaira.

      hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

ALHAKI NEH! (Page 1)

🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸

*ALHAKI NEH!*

🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋🌸🦋

® *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ŧɧɛ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

By the applomb writer: *Hamagee*

Wattpad @Hama_gee

Page 01

°
Da k'arfi ta bankad'o k'yauren d'akin umma tsohuwa tana banbami "wannan ai iskanci neh,ance miki tsufa hauka neh da zan sa miki abinci ki cakud'a ki barmun? Waye zaici sauran ki?".

Ummaa tsohuwa dake kwance ta mik'e zaune da k'yar tana fad'in "haba zuwaira kiyi hak'uri mana,wannan ai be kai abun ki tada hankalinki ba,ba'a cikin kwanon naci ba d'iba nayi,kuma abunda yasa kika ga ban cinye ba bana jin dad'i neh shiyasa!!"

Zuwaira tace "dalla rufan baki tsohuwar banza,mara imani mara tausayi dan bake kike cefanen ba shiyasa zakice haka ai,ance miki koh d'annaki da yake sayowa zan yarda yana mun irin wannan neh?"

Umma tsohuwa dai hak'uri tayi ta bata kun san ance fad'an daya fi k'arfinka sai ka zuba mishi ido kawai.
Tsaki Zuwaira tayi tareda fad'in "tsohuwar k'azama!".

Tayi ficewarta daga d'akin inda tabar Ummaa tsohuwa tanata faman neman gurin kwanciya dan ita koh kad'an abun be dameta ba dan idan ana sabo da wulak'anci toh ita kam ta riga da ta saba dashi.

Dan wannan kad'an neh daga aikin Zuwaira.Kullum haka suke da surkuwar tata,tsangwama,kyara,masifa da rashin ganin girma.

Zuwaira nah barin d'akin ta koma d'akinta inda ta tararda Aminu zaune cikin kashi,sai faman wasa dashi yake yi.

Wani tsaki ta jaa kafin ta k'arasa inda yake zaune ta d'aga shi daga cikin kashin sannan ta wanke mishi jiki ta gyara wajen.

Bayannan ta sa mishi wando tareda d'ora shi kan cinyarta ta soma bashi kunun data dama mishi shi kuma yana sha.

Sallamar meh gidan neh yasa ta d'ago kanta tareda ansawa,Mal.Mahdi yah k'araso tareda fad'in "sannu da gida!",tace "yauwa sannu".

Harya nemi guri zai zauna sai kuma yah tashi,d'akin Umma tsohuwa yah nufa inda yah sameta kwance kamar tana bacci,har zai juya sai yaji ta kira sunanshi "Mahdi!".

"Naam",yah amsa tareda juyowa yah shiga d'an bukkarta.Bayan yah shiga saiya nemi guri yah zauna kafin yace "yah jikin?"

Tace "da sauk'i"yace "toh madalla! Daman jikin nazo dubawa barinje inci abinci".

Umma tsohuwa tace "toh babu laifi",yah tashi yah fita yana toshe hancin shi.

Yana fitowa yazo yah tambayi Zuwaira ina abincin shi,tace dashi ya duba zaure.Zauren yah nufa yah d'auko abincin shi yazo yana ci.

Zuwaira ta dubeshi kafin tace "Mahdi nifa na fara gajiya da halin tsohuwar kah".

Loma na biyun da Mahdi bai kai ba kenan,yace "lafiya? Meya faru Zuwaira!".

Zuwaira ta fara kukan k'arya tana fad'in,"komai nayi ban fita ba? Ace ni kenan saidai ina bauta mata ita kuma tana wulak'anta nii,d'azu nah kai mata abinci,ta rasa abunda zata ceh mun sae zagi,ta uwa ta uba? Ga can abincin ma yadda na kai mata bata ciba,saita cakud'a shi ta bari,da nayi magana kuma saita fara zagina wai ai bani nake siyen abincin ba,kuma gidan d'anta neh dole kuma tayi abunda take so".

Ta share hawayen ta na k'arya kafin ta cigaba "ace baza taji tausayin ka ba duk irin wahalan da kake sha kafin ka samo mana abinda zamu ci,kamar ba ita ta haifeka ba?,nikam ban san yadda take so inyi mata,duka irin biyayyar da nake yi mata bata gani,in ta tashi zagina harda iyayenaaa".

Wani sabon kuka Zuwaira ta soma rerawa.Shi kuma Mahdi duk hankalinshi yah bi ya tashi dan inda abunda yafi tsana toh shine ya ga Zuwaira cikin damuwa.

Tashinda Mahdi yyi be nufa ko ina ba sai d'akin Umma yana huci kamar wanda zai je ya daketa,babu koh sallama ya fad'a mata cikin d'aki,ganin yanayin Mahdi yasa Umma tace "lafiya kuwa Mahdi?".

       hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 73)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*Wannan page d'in naku neh masoya wannan littafi,ina godiya da yadda kuke bin littafin,ILY'LL*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 73 💦💦

    Kowaccen su taji dad'in sannan rana da ta kasance ta aurensu amma banda Suhana,kasancewar ba wani sabon abu bane a wajenta kuma ma wanda ta auran ba sonshi takeyi ba,kawai dai biyayya tayi. Shi kuwa yana sonta har ranshi dan haka nema yake lallashinta. Washegari yayi introducing d'inta wa yaranshi gabad'ayan su kuma daga dukkanin alama bazata samu matsala daga garesu ba. Itama kuma tayi niyyar zama dasu tsakanin ta da Allah,babu ha'inci ko wani muzgunawa,shi kuma tasa ma ranta zatayi mishi biyayya irinta aure. Haka rayuwar Suhana ta cigaba kamar ba ita ba,iyayenta kuwa kullum cikin addu'a take yi musu.

★★★
Ko kun manta dasu Fahyim da Aasim da kuma matansu sannan qannensu? Ya kamata mu leqa su suma dan ganin yadda rayuwarsu ta kasance.

    Rayuwa mai cikeda jin dad'i da farin ciki sukeyi. A halin yanzu yaransu uku-uku dan a tare suke haihuwa wani ikon Allahn. Gidansu d'aya saidai kowa da side d'insu,koda yaushe suna tare kuma dan wajen aikin matayen d'aya haka ma mazajen. Yaransu ma makarantar su d'aya abinsu,kullum suna tare abin sha'awa.


    Watarana Aasim da Fahyim sun ziyarci wani abokin su wanda ya kusa yin aure a halinda ake ciki,shima tare suka taso saidai shi tun bayan gama secondary school d'insu suka rabu kasancewar ya koma Sokoto da zama,anan ya kammala karatun degree da masters d'inshi.


    Bayan sun kammala hiransu zasu tafi dan yamma yayi har magariba ya gabato. Fitowarsu keda wuya saiga wata mata na magana da almajiri,daga dukkan alamu abinci ta bashi. Basu kawo komai a ransu ba sukam,har sun saka kai zasu je wajen motarsu sai juyowarta ya hanasu,wa zasu gani banda Suhana. Kansu gabad'aya ya d'aure sai kallonta sukeyi. Abokin neh yace "wannan kallon fa? Kun Santa neh? Matar baba ceh fa",kowannensu ya kalli d'anuwan shi kafin suka maida kallon su ga Abokin.

   Suhana ceh tayi qarfin hali ta gaidasu,cikin yaqe suka amsa kafin ta wuce,bayan wucewar tane suke yima abokin nasu bayani,shine yace ai yanzu matar babanshi ce. Cikin mamaki suka koma gida,koda suka koma kowannen su saida yayi wa matarshi tad'in Suhanan. Suma matan sun yi mamaki matuqa dan basu tab'a kawowa  cewar Suhana zata nutsu haka ba harta iya auren tsoho kamar Alhj.Suhan,hakan ma ba wai wani kud'i yake dashi ba.


    A wajen Suhana kuwa kunya ce da nadamar abinda tayi wa Fahyim suka baibayeta,har dare tana cikin wannan tunanin har Alhj yaso ya fahimci damuwarta,koda ya tambayeta ce mishi tayi kanta na ciwo shiyasa. Washegari sun fita kasuwa suka had'u dasu Fahyim,a wannan karon harda su Abida da yaransu. Nanma Suhana bata ji dad'i ba ko kad'an,yaran kuwa ba qaramin sha'awa suka bata ba gashi yanzu ba iya haihuwa zatayi ba,ita dai ta cuce kanta kawai. Koda suka had'u gaisawa sukayi dake Alhj.Suhan yasan su daman suma kuma sun sanshi sosai. Haka rayuwar Suhana ta qare,babu iyenta,babu miji had'add'e mai kud'i,kuma babu haihuwa,what a pity life for her!

   Shin LAIFIN WANENE duk wa'yannan abubuwan da suka faru? Ina jiran feedback d'inku masu karatu. Anan na kawo qarshen wannan littafi me taken suna LAIFIN WAYE?, kuma ina roqon Allah yasa mu amfana dashi,mu cigaba da zuwa a littafaina na gaba wato 'ALHAKI NEH!, da kuma DA WATA QAWAR..'.

   Ina godiya ga Allah daya kawoni qarshen wannan littafi lafiya,kuma ina miqa godiya ta ga dukkanin masoya wannan littafi,taku har kullum Hama G Muh'd aka Hamagee.


      hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 72)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @Hama_gee

Page 72 💦💦

   Bayan Baffa yasha ruwan ne yake sanarda Alhj.Suhan abinda ke tafe shi,yace "wallahi bansan yarinyar nan na d'auke da wata cuta ba,shiyasa ma tun farko na amince maka akan ta",Alhj yace "to indai kuwa hakane fad'uwa tazo dai-dai da zama,baka da masaniya kan cewa cutar da ta kashe matata kenan? Ai ni tun farkon ma da nayi maka maganar yarinyar ba da gaske nayi maka ba saboda nasan ina d'uke da wannan cutar. To amma yanzu kaga na huta,Allah ya hore min mata".

   Ganin Baffa bai fahimci inda maganganun sa suka dosa ba yasa yayi mishi bayani dalla-dalla kan yadda akayi yake da cutar,Baffa yasha mamaki qwarai dan bai tab'a sanin cewar abokin nashi nada wannan cutar ba,saidai koma miye yayi godiya wa Allah tunda ya samu me auren Suhana. Bai bar gidan ba saida suka tsaida magana kan za'a had'a auren dana sauran yaran shi. A take ya bada sadakin Suhana tareda alqawarin nanda kwana biyu za'a kawo kayan auren Suhana dan already Alhj ya shirya ma yin aure,Matar ne da bai samu ba.

    Bayan Baffa ya sanar dashi date d'in da aka tsayar sai ya tafi bayan sunyi sallama,gameda Suhana ta tab'a yin aure kuma daman already Alhj ya sani,so ba wani abin b'oyewa bane. Ba qaramin farin ciki yayi ba,take ya fara sanarda 'yanuwa da abokan arziqi kan yayi mata,kowa murna yake taya shi barinma 'yanuwanshi. Ranan yayi bacci mai dad'in gaske.

    Washegari ya sayi waya tareda registering M.T.N line yasa a ciki da credit na dubu d'aya sannan yaje ma Suhana dashi dan Baffa yace batada waya kasancewar tun zuwanta gidan suka qwace. Koda suka gana da Suhana baiyi mata ba amma babu yadda ta iya hakan ta haqura dashi dan dole,kai kace an canza Suhana neh. Yarinyar da ada duk kud'in ka duk had'uwarka saita kusheka amma yau itace take zantawa da wannan tsofai-tsofai d'in a matsayin mijin da zata aura,duniya kenan.

     Biki sai matsowa yakeyi dan a yanzu sati guda ya rage a d'aura musu aure. Babu irin shirin da uwa keyi wa yaranta wanda Matar Baffa batayi wasu Ummu ba amma koda sau d'aya bata tab'a kwatanta gyara Suhana ba,a cewarta su sabin shiga neh ita kuwa babu abinda bata sani ba gameda aure dan haka bazata b'ata kud'inta da lokacinta wajen yi mata gyara ba. Saidai ko kad'an hakan bai damu Suhana ba kasancewar wanda zata auran ba wai son shi take ba balle tayi tunanin sashi farin ciki,kuma kamar yadda maman ke fad'in ita ba auren fari zatayi ba hakan ne.

    Kowacce daga cikinsu an kawo kayan aure da sadakin ta,sadakin su Ummu yafi na Suhana dan na Ummu 50k neh,saina Khadija wato Hadiza 40k,ita kuma Suhana 35k aka bada. Wajen kayan akwati kuwa na Suhana yafi nasu duka,kama daga kan akwatuna har kayan dake cikin akwatunan.

    Koda aka zo bikin komai tare akayi musu,'yanuwa da abokan arziqi kowa ya halarta. Kwana uku akayi ana shagali kafin aka kammala,kowaccen su aka kaita gidanta. Kayan garan da akayi ma su Ummu duk yafi na Suhana,hakan kuwa ko a gyalenta dan bata ma sani ba. Masu ganin gida kuwa kowa saida fad'i cewa gidan Suhana yafi kyau da girma,dan kafin auren saida Alhj ya sa aka gyara gidan. Side d'in yaran shi maza kuwa daban dake duk manya neh,d'ayan kanma ya kusa aure,d'aya kuma yana service dan ya kammala degree d'inshi. Yara matan kuwa anyi auren babbar,saura su biyu,d'aya na ss2 yanzu d'ayar kuma primary one ta shiga yanzu. Anyi aure dai hankalin kowa ya kwanta.

     hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 71)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 71 💦💦

   Bai jira su ba ya nemi taxi ya wuce gida kai tsaye,yana isa kuwa ya gabatar wa iyayen nasu da takardar. Hamdala sukayi da suka farga da wuri da aiki ya jiqa musu. Tambayar shi sukayi ina Fadeel d'in,yace musu yana zuwa sannan ya wuce ya fita. Sun jima suna juya maganar kafin daga bisani Baban yace zai je ya samu mahaifin ta anjima suyi magana dan wannan aure ba zai yiwu ba.

    Bayan tafiyar yayan Fadeel d'in sun jima a wajen kowa da irin tunanin da yakeyi. Daga qarshe dai ya d'auki Suhana ya mayar da ita gida sannan ya bata haquri kafin ya wuce ya tafi. Kai tsaye gida ya koma shima,nan mamansu ta sanarda shi duk abinda ke faruwa. Bai ji dad'in hakan ba sam dan harga Allah yana son Suhana,saidai duk yadda ya kai ga sonta ba zai yiwu ya gurb'anta rayuwar shi ba,shi kad'ai ya zauna yana tuno abubuwan da suka faru. A nan ya gano dalilin da yasa Suhana taqi amince mishi.

★★★
   Tunda Suhana ta koma gida take kuka,matar baffanta tayi-tayi da ita dan jin abinda ya faru amma taqi sanarda ita koma miye. Can Baffan ya dawo,shima yayi tambayar duniyar nan Amman taqi fad'i. Ana cikin hakan da yamma saiga su mahaifin Fadeel sunzo. Ba tareda b'ata lokaci ba sukayi sallama da Baffa ya fita yaje ya same su.

    Nan sukayi mishi bayanin komai,haquri ya shiga bayarwa dan shi ko kad'an bai san Suhana nada wata cuta ba ballantana ta HIV. Suka ce babu damuwa,daga bisani suka yi sallama tareda tafiya. Shikenan auren Suhana da Fadeel ya fasu,Allah ne ya taimake shi da yanzu ya zamo abin tausayi shima d'in.

    Idan ran Baffa yayi dubu to duka sun b'aci dan a ganin shi wannan abinda ya farun ba qaramin zubar mishi da mutunci bane. Sanin irin b'acin ranshi yasa baima shiga gidan ba kai tsaye ya wuce gidan wata yayarsu,ita Daddyn Suhana ke bi. Ya sanarda ita duk abinda ke faruwa,ita ma tayi baqin ciki matuqa saidai babu yadda suka iya,in hanunka ya b'aci ai baka yankewa ka yar,inji ta kenan.

    Da qyar dai Baffa ya haqura dan acewar shi bazai zauna da Suhana ba saidai a san yadda za ayi da ita kawai. Anan yake yi mata tad'in akwai wani abokin shi da yake ce mishi yana sonta dama dashi yake shirin had'ata,ganin zuwan Fadeel ne yasa ya jinkirta maganar. Amma yanzu shima d'in dole ya sanarda shi gaskiya dan inya zo daga baya ya gano to abin ba zaiyi kyau ba.

    Bayan ya bar gidan kai tsaye gidan abokin nashi ya nufa,babu laifi abokin yana da d'an rufin asiri dai-dai gwargwado duk da ba wani babba bane a fannin kasuwancin amma asirin shi a rufe yake. Har cikin palourn shi suka shiga kafin suka gaisa,Alhj.Suhan Abdullahi sunan shi kenan,shima d'in a Kaduna take da zama kuma nan ne tushensa. Matarshi d'aya me suna Rabi'atu wacce Allah yayi wa rasuwa shekaru uku kenan da suka wuce. Yaransu biyar da ita,biyu maza sai uku mata,qaramar cikin yanzu tanada shekaru biyar kenan a duniya.

    Haj.Rabi'atu ta kasance nurse dake aiki a babban asibitin Kaduna wato T.H,wata rana tsautsayi ya afka mata garin yin allura ma wata patient, wanda wannan patient d'in na d'auke da cutar HIV. A lokacin bata sani ba sai daga baya wanda already mijinta ya d'auka a wajenta a wannan lokacin. Haka tayi ta jinya har Allah ya d'auki ranta,wannan abin yasa Alhj.Suhan kasa yin aure har yau,maganar Suhana ma da yayi wa Baffa a wasa yayi mata dan babu yadda zaiyi ya aureta shi yanada cuta.

     hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 70)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 70 💦💦

Suna cikin hakan tace mishi zata shiga gida tana jin bacci,baiyi qoqarin hanata ba saima ce mata da yayi "it's ok my wife,have a lovely night",ba tareda tace wani abu ba ta wuce ta shiga gida abinta. Shi kuma cikin mota ya koma sannan ya tayar ya tafi gida kai tsaye,harya isa tunanin Suhana da irin maganganun da tayi mishi yake yi,saidai yasha alwashin wannan bazai sa shi ya rage sonda yake yi mata ba ko kad'an,itama kuwa yana addu'ar samun so daga gareta.


Ba qaramin rud'ani Suhana ta shiga ba kan lamarin Fadeel,gashi Baffa baida masaniya akan cewa she's HIV positive,shikenan ita kam asirin ta na neman tonuwa. Taso sanarda Baffa kan lamarin sau da dama dan ya dakatar da Fadeel daga neman ta karma abin yayi nisa amma ta kasa,ta rasa ta yadda zata b'ullo wa lamarin. Shima kan shi Fadeel d'in taso sanar dashi amma ta kasa,ta rasa yadda zata yi dai a yanzu,saidai a kullum addu'ar ta itace Allah ya kawo mata mafita cikin gaggawa.


Ana cikin haka har saura watanni biyu ayi auren su Suhana,gabad'aya fanni biyun sai shirye-shirye sukeyi. Saidai har yau Suhana bata yadda da cewa zata aure Fadeel ba,hasalima harta fito ta fad'a ma Baffa cewa bazata iya auren shi ba duk da bata iya sanar dashi dalilinta ba. Zaginta yayi tareda qara tabbatar mata da cewa ko taqi kota so saita aure shi in kuma ba haka ba to zai had'a ta da son ranshi kuma hakan ba zaiyi mata dad'i ba.



Gabad'aya Suhana ta rame ta rasa yadda zatayi da wannan maganar,kullum cikin tunanin ta inda zata b'ullo wa lamarin takeyi,saidai a koda yaushe tayi qoqarin samo mafita sai taga abin bai yiwu ba. Ana cikin haka watarana iyayen Fadeel suka matsa akan suje asibiti ayi test tunda biki ya kusa kada azo ayi wani abun d'an dana sani. Babu yadda Fadeel baiyi dasu ba kan su bari shi yasan babu wata matsala dan ya yadda da ita,kuma koma akwai shi baya son sani.


Amma ina iyayen shi suka qi da hakan,qarshe dai a dolen shi ya yarda suje ayi test d'in. Iyayen sun san zai iya baije ba yace musu yaje,hakan yasa aka had'a shi da babba,tare suka je gidansu Suhanan ma. Bayan sun nemi izinin Baffa ya amince sai suka tafi. Tunda Suhana taji hakan tasan cewa duk wata alaqar dake tsakanin su tazo qarshe dan babu makawa tasan in dai suka ji wannan magana to fasawa za suyi. Ta wani wajen taji dad'in hakan,ta wani wurin kuwa bata ji ba saboda tasan dole asirinta ya tonu a cikin 'yanuwanta,amma taji dad'i daya kasance Fadeel zai kub'uta daga wannan ciwon.


Suna isa asibitin ba tareda b'ata lokaci ba aka fara yin test d'in,bayan wani d'an lokaci kuwa result ya kammalu. Koda zo miqa ma Fadeel result d'in,yayan shi bai bari an bashi ba ya karb'a. Nan ya shiga karantawa kuwa,ganin bai fahimci abinda ke cikin dakardar ba yasa ya je gurin likitan daya rubuta musu test d'in tun farko ya bashi papern.


Bayan ya karb'a saiya shiga dubawa kafin daga qarshe ya rubuta musu result d'in in detail ya bashi a hannun shi,bayan nan yace mishi "akwai matsala a auren nan da ake shirin yi because macen tana da HIV". Godiya yayi mishi kafin ya fita,kallo d'aya yayi musu kafin ya wuce yayi tafiyar shi ya barsu a wajen suna tsaye.


www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 69)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 69 💦💦

Ba qaramin mamaki maganganun ta suka bashi ba,maybe wani yayi breaking heart d'inda ne shiyasa take gudun soyayya,a ranshi ya fad'a. Komawa cikin mota yayi ya kunna ya tafi da niyyar zai dawo dan shikam yaga abinda yake so kuma baya tunanin akwai abinda zai hana shi aurenta saidai wani ikon Allahn. Yana komawa gida ya sanar wa iyayen shi abinda yake ciki,nan mahaifin shi yayi mishi alqawarin shige mishi gaba indai sun bincika sun ga asalinta nada kyau,hakan ba qaramin dad'i yayi mishi ba.


Suhana kuwa bata shiga cikin gidan ba saita tsaya a soron gidan tana kuka. Saida ta gama kukanta sannan ta shiga,tana shiga kuwa idon kowa ya dawo kanta cikeda tambaya. Baffanta yace "wanene?",tace "wani d'an makarantar mune tun ina university na nan garin",baffan yace "haka zaki qare ai,saidai d'an makaranta ba dai miji ba,toni wallahi na gaji da ciyar dake idan kika kasa auruwa duk wanda naga yamun dashi zan had'aki kinji na gaya miki,daman akwai wanda yamun maganarki ma".


Matar shice tace "sosai ma kuwa,kina gani qannan kin nanma auren su za ayi nan da wata biyar,gara ma ki samu ki fidda miji in kuma ba haka ba had'aki zamuyi da wanda Babbanfi yake so dan tare zamu aurar daku ehe,bazamu rabuda namu yaran sannan ke mu zauna dake ba",duk maganganun nan da sukeyi idon Suhana na qasa tana kuka.


Washegari da rana wajen qarfe biyu saiga mahaifin mutumin jiyan nan da wasu maza su uku. Sallama suka sa akayi musu da Baffa,sunci sa'a kuwa bai fita ba yana nan. Ba tareda b'ata lokaci ba kuwa ya fita,koda suka sanar dashi dalilin zuwansu yayi maraba da hakan sannan yayi musu alqawarin babu wata matsala,sannan yana son ganin yaron koda anjima neh. Sunyi farin ciki da jin hakan sannan sukayi godiya suka tafi ko ruwa basu yadda sun sha ba,a cewar su suna sauri neh.


Da daddare kuwa saiga mutumin nan,koda Baffa ya fito gaishe shi yayi shi kuma ya amsa cikin mutuntawa,ya tambayeshi "kaine Fadeel koh?",yace "nine Baba",Baffa yace "to madallah,daman nasa a turo mun kaine dan naji daga bakinka,shin kanason Suhana?",wani farin ciki Fadeel yaji kasancewar bai tab'a jin sunanta ba sai yanzu,a ranshi yace suna mai dad'i. A fili kuma ya amsa ma Baffa tambayar shi "eh ina sonta hasalima nina tura azo a nema mun izinin nemanta",Baffa yace "to babu matsala,mun riga da munyi magana da magabatanka akan nan da watanni biyar dama nake so na aurar dasu itada qannenta guda biyu".


Fadeel yace "babu komai duk an min bayani",Baffa yace "to madalla,barin shiga saina aiko maka da ita",Fadeel yace "to na gode Baba,a huta lafiya",baffa yace "yauwa",tareda komawa ciki. Befi shigarshi da minti uku ba saiga Suhana,tana tafe kamar wacce qwai ya fashe ma a ciki. Da sallama ta isa wajen shi,shi kuma ya amsa tareda sakar mata da murmushi kamar koda yaushe in sun had'u.


Cikin zolaya yace "amaryata ta kaina!",bata ce mishi komai ba,shima kuma hakan bai dame shiba. Bayan d'an wani lokaci jin shirun yayi yawa yasa Fadeel ya kira sunanta "Suhana!",ba tareda ta amsa ba ta juyo ta kalleshi,cigaba yayi "meyasa baki sona?". Sam ita har a ranta ba wai bata sonshi bane saidai cutar da take d'auke da ita ne tasan in har yaji to babu makawa fasa aurenta zaiyi,itama kuma bata son ta cutar dashi dan haka ta d'au aniyar dakatar dashi koda kuwa ta halin qaqa ne.


www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 68)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 68 💦💦

    Sai a yanzu ta fahimci cewa Suby ba qawar arziqi bace,tunda a da bata guje taba sai yanzu da taga rayuwarta ta zamo miserable. Amma hakan ya qara koya mata hankali neh,a yanzu tasan irin mutanen da zata ringa huld'a dasu kuma tasan yadda zata bi dasu. Har yau a kullum cikin yima iyayenta addu'a takeyi dan samun rahamar ubangiji. Abinda zai bama mai karatu mamaki kuma islamiya Suhana ta koma a yanzu,dan baffanta yace shi ba ayi mishi zaman banza a gida,indai yarinya ba aure tayi ba to dolenta ta ringa zuwa islamiya,zuwanta islamiyar ba qaramin taimaka mata yake yi ba ta fanni daban-daban.

   Na farko tana samun ilimi ga abinda ya kamata ta sansu da bata sani na,na biyu yana d'ebe mata kewa dan idan tana makarantar ji take kamar kada a tashi ma ta dawo gidan,gashi yanzu Alhamdulillah tana yin sallah. Watarana da safe ta fito zata makarantar tanata sauri kasancewar tayi latti dan saida ta tsaya yin aikin gida kafin ta fita. Tana tafe tana tuntub'e dan bata son tayi latti sosai.

   Horn d'in mota ta jiyo daga bayanta amma bata ko juya ba,saima saurin da ta qara. Shi kuma me motar sai sake horn d'in yakeyi,ganin bazata tsaya ba yasa ya qara gudu yazo gabanta ya tsaya da motar,kafin ta canza hanya ta tafi harya fito daga cikin motar da saurin shi. Kafin ma yayi mata magana tace "lafiya mallam,baka ganin already nayi late neh?". Murmushi yayi kafin yace "haba baiwar Allah,tambayar ki fa kawai zanyi. Gidanku nake son in sani so that anjima in kin dawo saina zo muyi magana dan bai kamata muyi ta anan ba kinga ma kina sauri",da qyar ta yadda tayi mishi kwatancen gidan hakan ma dan taga zai b'ata mata lokaci neh.

     Around 5 na yamma saiga mutumin nan yazo gidansu Suhana,yaro ya aika cikin gidan akan yayi mishi kiranta,kwatance yayi ma yaron dan baima san sunanta kasancewar a hanya suka gamu. Yaron kuwa ya gane wacce aka aike shi ya kira d'in,dama 'yanmata uku ne a gidan,Hadiza da Ummu-khulsum su yaran baffan Suhana neh,sai kuma Suhana da ta cika ta ukun,dukkan su chocolate complexion ne dasu so Suhana ce kad'ai fara shiyasa yaron yasan wacce ake kiran.

    Suhana na zaune ta kammala sharan tsakar gida kenan saiga yaron nan da aka aiko,ita kanma ta manta cewa sunyi wata magana da wani d'azu. Yaron yace "wai ana magana da baquwar gidannan",daga ji sun san da Suhana akeyi. Baffan ne ya daka mata tsawa "baki ji bane ko so kike sai an roqe ki da ki fita?",matarshi tace "inaga". Tashi Suhana tayi da sanyin jiki ta shiga d'aki inda ta d'auko hijabinta ta nufi hanyar fita wajen bada sonta ba.

    A jingine jikin motar shi ta same shi yana jiran fitowar ta,tana fitowa kuwa ya sakar mata murmushi,ita kuwa d'aure fuska tayi kafin ta qarasa. Ce mishi tayi "wai lafiya mallam kake ta bina neh?",yace "lafiya klou". Tace "to fad'i abinda ke tafe da kai inada abinyi". Yadda take masifa qara burgeshi yakeyi,smiling yayi tareda fad'in "idan kin so ma yanzu zan barki ki tafi,matuqar zaki bani abinda nazo nema".

    Da sauri da juyo dan ta matsu ya barta ta shiga gida tace "fad'i menene?",yace "tun d'azu dana ganki naji kin kwanta mun a rai,kinyi daidai da irin macen dana ke son ta zama matata,sannan...",bai qarasa ba ta katse shi "dakata mallam,waye yace maka nayi daidai da irin Matar da kke so? To karka yadda idanunka su rud'i zuciyarka a kaina,ban dace da kai ba",tana kaiwa nan ta tafi ta barshi a gurin cikin kuka dan ya sosa mata inda yake mata qaiqayi ne.

    www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 67)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 67 💦💦

    Rungume Mommyn tayi tana cigaba da kuka,bayan d'an qanqanin lokaci Mommy tasa hannu ta d'agota tareda share mata hawayen dake ta faman zabarya a fuskarta. Tace mata "be strong my child,you ain't a small kid anymore don't you know?,you have to be strong and patient kinji,Allahn daya had'a mu ya kuma raba mu shi zai sake had'a mu kinji",sam Suhana bata fahimci inda zance Mommy ya dosa ba hasalima kanta ya d'aure neh. Mommy ta cigaba "na sa an kira ki dan nayi miki nasiha kan kibi rayuwa a sannu,hanyar da muka d'ora ki daga farko ba mai b'ullewa bace dan haka ina roqonki da sauya ko zamu samu Rahamar ubangijinmu nida mahaifinki",daga nan Mommy ta shiga kuka.

    Itama Suhanan kuka take yi dan gabad'aya Mommy ta d'aure mata kai,da qyar ta iya daidaita kanta tace "naji Mommy amma bana so kina irin wannan maganan please, yana d'aga mun hankali it seems kamar you want to leave me as well",murmushi mai cikeda maganganu a cikin shi. Tace "you're not a child as I mentioned earlier, nasan zaki iya kulawa da kanki ko bayan raina dan bana ji a jikina zan kai labari,ke dai kawai be a good child and always pray to your parents kinji". Hawaye neh yake ta zuba shar-shar daga idon Mommy,tayi nadamar duk wani abinda tayi a rayuwa,tasan cewa bata kyauta wa Suhana ba dan duk halinda take a yau akwai nata kamishon.

    Washegari da yamma Allah yayi wa Mommy cikawa,sai dai tayi kyakyawan cikawa dan da kalmar shahada ta rasu. Suhana tasha kuka kuma tana kan sha,bayan anyi wa Mommyn wanka aka ajiye ta wa 'yanuwa su gama mata addu'ar da zasuyi kafin aje ayi mata sallah a birne gawar. A wajen ma ba qaramin kuka Suhana tayi ba dan daga qarshe kanma d'agata akayi a wajen.

    Days ltr,
Lokacin da dangin Mommy suka zo tafiya taso ta bisu dan tasan indai ta zauna a wajen dangin Mahaifin ta sai sun qarasa ta ganin cin mutuncin da suka tayi wa Mommy kafin ta rasu. Koda tayi qoqarin bin nasu sai dangin Daddyn sukayi uwa sukayi mad'aukiya akan ba inda zata,gidan wani qanin Daddy zata koma da zama. Dangin Mommy basuyi musu ba dan sun san qarfin dangin uba akan na uwa.

   Bayan wasu kwanaki tas ta tattara kayanta ta koma gidan immediate qanin Daddy,tsakanin shi da Daddyn bai wuce shekaru biyu da rabi ba. Tun ranar data koma gidan ta fara fuskantar rayuwar qunci,kun san dan idan mahaifinka yanada dukiya akan sauran danginshi,to dole a cikin dangin nashi akwai wanda suke jin haushin hakan,bama haushin sa shi kad'ai ba hatta iyalanshi ma basu bari ba,Allah ya kyauta.

   Bayan an raba gado na Suhana a wajen shi yake,yace shi dai duk rintsi ba zai ci hakkin maraya ba amma kuma ba yanzu zai damqa mata ba sai randa tayi aure. Haka ta cigaba da rayuwar ta cikin qunci da kewar iyayenta,abinka da bata saba da wahalar ba. Gashi matar baffan nata azababbiya ce dan shima kanshi bata barshi ba balle kuma Suhana,kullum cikin bauta take yi musu itada yaranta. Shima kuma babu abinda yake cewa gameda hakan.

   A sannu a hankali Suhana ta fara sabawa da rayuwar ta a haka,sai dai kafin ta saba tasha wahala sosai duk da ance ba'a sabo da wahala amma ita kam har ya bi jikinta,Suby qawarta kuwa tuni ta fita harqarta ko waya bata yi mata,idan ta kira ma bata amsawa. Kai qarshe ma blocking d'inta tayi a duk wata kafa na sada zumunta sannan tasa ta a black list yadda inma ta kira ba shiga zaiyi ba. Hakan ko ba qaramin d'agama Suhana hankali yakeyi ba.

    www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 66)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 66 💦💦

    Waje suka samu suka zauna sannan Mommy ta dubi Suhana tace "Allah yayi wa mahaifin ki rasuwa Suhana",wani irin jiri ne ya kusa yarda Suhana danma a zaune take,abinka da tsakanin d'a da mahaifi sai Allah. Kukan nema ya gagareta sai kawai ta koma ta d'an kishingid'a a kan kujerar. Suby kuwa salati ta shiga yi tana fad'in "Allah ya gafarta mishi yasa ya huta,sannan Allah yayi mishi rahama mu kuma in tamu tazo yasa mu cika da imani",Mommy ce ta amsa mata da "ameen" dan Suhana kam tana ta kanta neh.

   Ganin yadda a lokaci guda duk Suhana ta kid'ime yasa Suby ta shiga bata baki "haba Suhana mutuwa fa tana kan kowa,daurewa zakiyi,kuma ma insha Allahu ya tafi a sa'a sakamakon irin wahalhalu na jinya da yayi ta sha d'innan". Suhana bata ko amsa mata ba,can ta fashe da kuka mai tsanani abinka da dama ba islamiya taje ba ballantana tasan cewa haramun neh kuka me had'e da ihu ko hayaniya ga mamaci. Tana yi Suby na bata haquri,harta d'an sassauta muryarta dan muryar ta riga da ta dishe.

    Can aka fara shigo musu ta'aziyya,kama daga 'yan anguwa zuwa 'yanuwan Daddyn. A cikin su kuwa akwai masu yima Mommy habaici dama ba sonta suke yi ba asali,kasancewar Daddy nada kud'i suna cin arziqi a wajen shi yasa basuyi mata ido da ido. Daga cikinsu kuwa akwai masu fad'in ai itace ta kashe shi dan taci dukiya.

    Wasu na fad'in ita ce ta nakasa shi tun farko dan taci arziqi sai kuma yazo ya talauce,babu abinda basu fad'a mata ba na b'atanci amma shiru kake ji dan ko Suhana bata tanka musu ba balle Mommyn. Kaf abincin gidan saida aka dafe su wa 'yan zaman makoki,a cikin qannen Daddy kuwa akwai wa'yinda musamman suka baro gidajen su suka dawo gidan suna kwana tsabagen neman ayi.

   Banda hantara kuwa babu abinda sukeyi wa Mommy da Suhana,ana haka har anyi sadakar bakwai. Maimakon su tafi saima canjen rana da sukeyi a tsakanin su,idan guda biyu suka kwana biyu sai su koma gida wasu biyun su dawo suma su kwana biyu,sunyi matuqar saka Mommy a gaba hakan yasa rana a tsaka ta yanki jiki ta fad'i,daga dukkanin alamu ciwon tane ya tashi.

    Suhana da taimakon Suby neh suka kaita asibiti dan in don ta qannen Daddy neh sai dai ta mutu a wajen dan ko d'aga ta baza suyi ba balle su kaita asibiti. Koda suka isa asibitin taimakon gaggawa aka yi mata dan direct to imagency aka tura ta,Suhana kuwa banda kuka babu abinda take yi. Suby ceh me d'an rarrashinta,itama d'in gabad'aya tausayin Suhana take yi.

    Bayan kaman twenty minutes da karb'an Mommy sai ga wata nurse da hanzarinta,ganin su Suhana a tsaye yasa ta tambayesu ko sune suka kawo mara lafiya yanzu,sukace sune. Nurse d'in saita ce "ok,who's the woman's daughter amongs you? Her attention is needed by the patient please",tana kaiwa ta juya ta fara tafiya.

    Nan Suhana tabi bayanta da sauri,cikin qanqanin lokaci sai gasu nan a d'akin da Mommy take,da sauri Suhana ta qaraso inda Mommyn take ganin idonta biyu neh lokacin. Kuka mai tsanani ta shiga yi tana fad'in "get well soon Mom please,I don't want to miss you even for a second from now on I promise, don't leave me the way Dad passed away",kuka take kamar yarinya tana maganganu. Mommy ta tausaya ma Suhana sosai,dafa ta tayi sannan Suhanan ta d'ago kanta tana kallon Mommyn.

    www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 65)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 65 💦💦

   Can ta dubi agogon wayanta sai taga qarfe goma sha d'aya har ya wuce. A nan ne ta fara zargin ko dai Mommy ta kai Daddyn India neh,amma a ina zata samu wannan kud'in. Can dai data gaji saita koma d'aki ta kwanta,bata jima ba nan ma tayi bacci. Washegari sai qarfe goma na safe ta tashi, babu batun sallahn asuba ta tashi ta shiga toilet tayi brush sannan tayi wanka ta fito.

    Wayan Suby ta kira inda suka sha hirarsu,anan nema Suby take ce mata zata zo garin gobe dan a yanzu ta koma gida gun iyayenta daman school ne ya kawo ta nan Kaduna. Suhana taji dad'in batun qawarta sosai dan sun jima basu ga juna ba sai a waya,bayan sun gama wayan Suhana tayi hanging.

★★★
India,
    Wanka akayi wa gawan Daddy kasancewar sun san cewa bashida 'yanuwa a nan kusa kuma akwai musulmai a wajen. Bayan nan aka yi mishi sallah da dai sauran hidimar da ake yi wa mutum idan ya mutu,daga nan aka kai shi aka binne. Shikenan shima tashi ta qare,Allah kasa mu gama da duniya lafiya,ameen.

    Washegari da safe Mommy ta farka garau,sai dai inta tuna da cewa babu Daddy a doron qasa saita fashe da kuka mai tsanani. Tana cikin wannan yanayin Likitan dake dubata yazo ganin yanayin jikin nata,nan ya shiga lallashinta kan ta daina d'aga hankalinta,mutuwa kowa yasani tana kanshi,yau mune gobe kuma ba mu bane so she should let things past.

    Koda aka sallameta bata koma gida a ranan ba sai gobe zata koma,bayan ta kammala biyan asibiti kud'in su saita nemi hotel inda zata kwana gobe saita wuce. Babu irin tunanin da bata yi ba gashi ita kad'an ta kamar rai,har yanzu bata sanarda kowa kan rasuwar Daddy ba tafi so saita koma gida kawai dan jimamin fad'in ma takeyi.

    Washegari ta tattara kayanta ta dawo gida,bata tsaya ko'ina ba kuwa sai gida. Lokacin da ta iso Suhana kuma bata gidan,ko ina taje? Sai Allah. Wanka Mommy tayi kafin tayi sallah,bayan nan ta fito ta nemi abu taci. Daga nan kuma ta shiga tura messages ma 'yanuwa da abokan arziqi kan cewa Daddy Allah yayi mishi rasuwa,bayan ta gama saita ajiye wayar ta d'an kishingid'a.

     Babu abinda take banda aikin kuka,duk lokacin da ta tuno da Daddy sai taji kewarshi ya cikata,barinma idan ta tuno yadda suke rayuwar su a da. Tasha kuka harta gode Allah dan da ganin ta kasan ta jima tana kuka saboda gabad'aya idonta sun kumbura sunyi jaa. Addu'a ta shiga yi ma Daddy na samun rahamar ubangiji,nima nace Allah ya jiqan Daddy,ameen.

    Can Mommy ta juyo hayaniya kuma kaman a cikin gidan neh,tashi tayi taje ta duba, bud'e qofarta kenan sai tayi ido biyu da Suhana,ga kuma Suby a bayanta daga dukkan alamu ita taje taryowa. Ganin yadda fuskar Mommy ya sauya,ga idonta sun kumburo sunyi jaa dasu yasa Suhana cikin tashin hankali,daga gani tasan ba lafiya ba. Da qyar ta iya fad'in "Mommy lafiya? Ina kka je tun shekaran jiya ban ganki ba ? Ina Daddyn yake,kun dawo tare neh?".

     A cikin wa'yannan jerin tambayoyin babu wanda Mommy keda niyyar amsawa,komawa ciki kawai tayi tana share qwalla. Suma cikin suka biyota,Suhana ta zaci akan maganar da sukayi neh dan haka ta shiga bata haquri "Mommy am sorry please, ban fad'i hakan da niyya ba ko kuma dan ban damu daku ba,nayi hakan ne dan ganin wahala kawai za ayi ta sha. Shi bai samu lafiya ba mu kuma mu qare cikin babu,amma kiyi haquri yanzu na amince a fitar dashi d'in,Mommy ki min magana mana".

     www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 64)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 64 💦💦

   Abin ya bata mamaki,bata tab'a tsammanin Suhana zata ce hakan ba. Tace "haba Suhana, yanzu haka kike so mu zauna muna kallon Daddyn ki?". Suhana tace "oho,ni dai bazan iya bada wasu kud'in bane kuma babu gidan da za'a saida,ni ban hanaki kai mijinki ayi mishi jinya ba ni dai kawai na gaji da zubar da kud'i a asara ehe!". Mommy tace "yanzu mahaifin naki ne asarar".


    Suhana ta ja tsaki ta bar wajen ma,gida ta koma inda ta d'an dafa indomie taci daman yunwa take ji,bayan nan saita kwanta sai bacci. Mommy kuwa kasa d'aukanta qafafunta sukayi a wajen ta zube tana kuka me cikeda dana sani wanda mallam bahaushe yace qeya ceh. Tama rasa ta inda zata b'ullowa lamarin,daga qarshe dai ta yanke shawarar cin bashi a banki dan nan ne kawae zata samu biyan buqatar ta a yanzu,tashi tayi ta nufi banki inda ta samu taci bashin kud'in sannan tayi musu shirye-shirye akan anjima da daddare zasu wuce India.

    A asibitin ta bar Daddy bayan ta roqi alfarmar cewa su riqe shi kafin lokacin tafiyar tasu tayi dan yanzu idan ta maida shi gida ma bata san yadda zatayi dashi ba gwara yana gurin likitoci. Bayan ta koma gida kaya ta d'ayan had'a musu wanda basu wuce set biyu ba kowannen su,koda ta gama abinda zatayi zuwa qarfe biyar ta fito,har a lokacin Suhana na kwance tana ta sharar bacci kamar wacce bata san me ake kira da matsala ba,girgiza kai kawai Mommy tayi sannan ta fice.


    A ranta tana mugun son Suhana hakan yake hana idan tayi LAIFI tayi mata fad'a wanda hakan ba qaramin kuskure bane. Asibitin ta koma inda ta zauna a kusada Daddy tana ta qare mishi kallo. Saida lokacin tafiyar su ya kusa kafin suka bar asibitin,suna isa airport kuwa ana kiran sunan su sai suka shiga jirgi. Qarfe bakwai daidai jirginsu ya d'aga.


    Suna isa India kai tsaye asibitin suka nufa inda Likitoci suka karb'i Daddy cikin gaggawa suka shiga duba shi. Anan ne suka gano cewa allurar da akayi mishi jiya tayi mishi qarfi ainun wanda yinta ya katse hanyar yawon jikin a system d'in shi. A halinda ake ciki dai Allah yayi wa Daddy rasuwa run a cikin jirgin,kasancewar dama ba motsi yakeyi ba yasa ko kad'an Mommy bata fahimci hakan ba,sai dai babu yadda aka iya da ikon Allah,shine mahaliccin rai kuma shike d'aukan na wanda yaso kuma a lokacin daya so,sannan ta yadda yaso,Allah ya gafarta ma Daddy shine fatan mu.

    Koda aka sanarma Mommy a wajen ta yanki jiki ta fad'i sumammiya,nan aka ciccib'eta sai sick bay inda aka bata immediate treatment, Allah sarki Mommy bugawa zuciyar ta tayi a halin yanzu ta kamu da ciwon zuciya. Bayan an gama treating d'inta dan harta farfad'o ma sai akayi mata alluran bacci tareda d'aura mata drip sannan aka barta ta huta da fatan in ta farfad'o shikenan ta warware.


★★★
Sai can dare Suhana ta farka daga baccin da takeyi tun azahar har anyi sallahn isha yanzu. Tana tashi bata tsaya ko'ina ba sai toilet, wanka tayi sannan ta fito ko sallah babu,daman ganin idon iyayen ne yake sata wani lokacin tayi sallahn. D'akinsu ta nufa inda ta tarar har yanzu Mommy bata dawo ba,a ranta tace ko lafiya oho. Fita tayi ta koma palourn inda ta d'au wayarta ta shiga yin chatting,wanda rabonta da yi ya d'an kwana biyi,cikin jin dad'i take abinta.

    www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 63)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 63 💦💦

    Suna zaune kowa da irin tunanin da yakeyi Suhana tace wa Mommy "yanzu Mommy haka zamu cigaba da zama kaman bamu da 'yanuwa da zasu taimaka mana,infa muka cigaba da zama a haka to wallahi sai mun wayi gari sisi ma bamu dashi so gwanda kawai mu san nayi",Mommy tace "Suhana kenan,kema kin san yanzu 'yanuwana ba kaman da bane,kowa na fama da kanshi to balle kuma dangin mahaifinki,ke kin san komai ai kin san cewa dashi suka dogara,koma ba haka ba idan yau aka taimaka mana ai gobe za a gaji damu ko".


    Suhana taja wani ajiyar zuciya kafin tace "hakane amma gaskiya abin ya fara yin yawa,duba fa,yanzu daga ni har ke babu me kud'i in banda canjin daya rage d'innan ba",Mommy tace "to yaya zamuyi neh,ai dai baza mu barshi ya mutu da ciwon ba ko,dolenmu muyi mishi magani koda hakan na nufin tsiyacewar mune gabad'aya". Suhana ta juyo ta kalleta alamar rashin yadda da maganar ta sannan ta juya kai,daga nan bata sake cewa qala ba,itama Mommyn bata sake maganar ba.

    Washegari tsaf suka shirya da sassafe suka nufi asibitin,koda suka isa ba'a bari sun ganshi ba dan bai farka ba tukunna kuma so ake yi ya tashi da kanshi,ba a son a tashe shi. Guri suka nema suka zauna inda kowaccen su ke tunani dan yanzu tunani ya zamo musu kaman jiki. Suhana kuwa ba komai take qullawa a ranta ba illa ta gaji da kashe ma Daddy kud'i kuma kullum abu guda babu wani d'an cigaba.

    Har wajen qarfe sha biyu na rana bai farka ba,hakan ya bama Likitocin mamaki dan by now ya kamata ace ya d'an dawo daidai ma,wata allura sukayi mishi wacce tasa ya farka babu shiri. Instead of a samu cigaba tunda anyi aikin saima qaruwa da lamarin yayi fiyeda da d'inma. Ganin hakan yasa suka bama su Mommy a fidda shi waje kawai dan a halin yanzu basu san abinda zasu sake yi mishi ba.

    Koda aka fad'a musu hakan instead of them su yadda da qaddara sai Suhana tayi caraf tace "why doctor? Why?,kusan cewa fa you people can't cure him to miyesa kuka ci mana kud'i,yanzu kun san muna da kud'in fidda shi wake ko bamu dashi neh?". Likitan yace "sai dai haquri dan muma bamu san hakan abin zai dawo ba,dama kun hanzarta kun san nayi ne because the patient is in a critical condition now, you have less time", yana kaiwa nan ya tafi ya basu a wajen.


    In banda salati da koke-koke babu abinda Mommy keyi. Suhana ce ta dubeta tace "to kinji fa,ni wallahi na gaji haka,ya isheni". Mommy tace "yanzu ki kawo sauran kud'ad'en wajenki mana a samu ayi wasu shirye-shiryen in yaso wanda ya gagara sai mu saida gidan da muke ciki in yaso mu nemi koda d'aki d'aya ne da palour,sai kitchen da toilet".


Wani irin kallo Suhana ta zuba ma Mommy kafin tayi commenting "haba dai mu saida gida",Mommy tace "to yaya zamuyi shi kad'ai ya rage mana,ko kinada wata dabarar ce?". Suhana tace "ai dabarar kenan a barshi a gida a cigaba da yi mishi addu'a ko zai samu sauqi dan wallahi ni yanzu na gaji,kud'in ma da kike cewa in bada bazan iya badawa ba gaskiya",baki sake Mommy take kallon Suhana.

    www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

LAIFIN WAYE? (Page 62)

💦 💦💦💦 💦
*LAIFIN WAYE??*
💦💦💦 💦💦💦

_Written by the Aplomb writer: *Hamagee*_

*In devotion to Maman Saif*
💦

Wattpad @ Hama_gee

Page 62 💦💦

   Hotel ta kama sannan ta fara shirye-shiryen komawa gida,nan da jibi take son ta koma. Tana kwance a d'akin da ta kama ta d'au wayarta ta shiga kiran Mommy,bata b'oye mata komai ba harta zuwa gurin Michael da tayi da irin labarin da ta jiyo har zuwa kama d'akin da tayi,daga qarshe ta qara mata da cewa jibi tana nan dawowa. Babu yadda Mommy ta iya sai haquri tunda koma miye ya faru a yau tanada LAIFI itama.

    2days after,
Qarfe shabiyi yayi ma Suhana a Nigeria dan morning flight tabi,wajen qarfe d'aya kuwa ta isa gida da d'an jakar kayanta qarama kasancewar duk kayayyakin ta na Uganda dan basu barta ta fita da ko d'aya ba sai na jikinta kawai. Sun sha kukan su itada Mommy har sun gaji,saidai kukan nasu ba abinda zai qare su dashi.

    Suhana na zaune a palour ta had'a uban tagumi in banda tunani babu abinda takeyi. Mommy ce ta fito daga d'akin su a hanzarce,"Suhana!",amma shiru dan Suhana bata ma san inda take ba balle tasan ana mata magana. Qarasowa Mommy tayi ta d'an bugeta "keh Suhana",sai a lokacin tasan da Mommy na wajen.

   Cikin hanzari Mommy tace "kizo mu kai Daddyn ki asibiti jikin shi ya tashi,yanzu kije d'aki ki zauna a jikin shi inyaso ni kuma saina fita na nema mana koda me adaidaita ne",wani irin juyowa Suhana tayi ta kalli Mommy kafin tace "me adaidaita fa naji kince?",Mommy tace "eh mana,to Suhana in bamu nema ba munada mota ne?". Suhana tace "au yanzu daman ko motar hawa guda d'aya babu a gidan? To garage d'in can miye amfanin shi?".

    Mommy tace "haba Suhana,ina muka ga ta ajiye mota a gida bayan irin wahalan da muka sha a jinyar Daddyn ki,kina gani fa gidan da muke ciki ma saida muka saida,ga qaddarorin shi dama nawa da muka saida still jikin babu dad'i",Suhana ta tab'e baki kafin tace "je ki nemo amma taxi ba adaidaita sahunnan ba". Mommy tace "shikenan" sannan ta fita neman d'an taxi a waje.

      Nan Suhana ta nufi d'in inda ta taradda jikin Daddynta babu dad'i,sannu ta shiga yi mishi kafin Mommy ta dawo da me taxi har cikin gidan. Fito da Daddy sukayi suka sa shi a motar sannan suma suka shiga suka tafi. Suna isa kuwa aka karb'e shi sai emergency, allura sukayi mishi sannan ya d'an samu yayi bacci dan lokacin da suka kawo shi buge-buge yake tayi.

    An caje su kud'i kam ba na wasa ba dan a cewar Likitan aikin dashen qodar da akayi mishi bai zauna daidai ba so dole a daidaita mishi inba haka ba yana gama gocewa daga gurbinshi zai iya rasa ranshi,gashi aikin na gaggawa neh. Haka suka harhad'a kan kud'aden da suke dashi kama daga kan na Mommy wanda Suhana tayi ta turo mata harna Suhanan ita kanta. A yanzu basu da ajiyan kud'i daya wuce dubu d'ari,shima kuma dole zasu ringa saya mishi magunguna akai akai.

    A ranan da yamma akayi mishi aikin dan na gaggawa neh. Bayan aikin sai aka kaishi wani d'aki inda zai huta shi kad'ai dan ba a son ayi disturbing d'inshi daga nan zuwa gobe da safe aga yadda Allah zaiyi abin shi. Koda jin hakan sai su Mommy suka koma gida dan ko sun zauna ba shiga za'a barsu suyi ba,iyakaci Likitocin dake kula dashi neh suke leqawa time to time.

     www.hghausanovelseries.blogspot.com

Share:

Popular Posts

Translate

Archive

featured post

UNIVERSITY GIRL Final episode(Chapter thirty)

Powered by Blogger.

Contact Form

Name

Email *

Message *

Blog Archive